DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar kwadago ta NLC ta fitar da sanarwar yajin aiki nan da mako biyu.

-

 Kungiyar kwadago ta NLC ta fitar da sanarwar yajin aiki nan da mako biyu. 

Google search engine

Kungiyoyin kwadagon NLC da TUC sun fitar da sanarwar tsunduma yajin aiki nan da kwanaki 14 masu zuwa muddin gwamnatin tarayya ba ta yi abin da ya dace game da tsadar rayuwa da ‘yan kasa ke ciki.

Sanarwar ta kuma ce kungiyoyin sun yanke wannan shawarar ne saboda gazawar gwamnatin Bola Tinubu na aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma a ranar 2 ga Oktoba, 2023, biyo bayan cire tallafin da aka yi wa man fetur.

Shugabannin NLC da TUC sun bayyana bakin cikinsu cewa duk da kokarin da kungiyoyin kwadago ke yi na tabbatar da zaman lafiya a tsakanin ma’aikatan gwamnati, da alama ita gwamnatin ba ta damu da dimbin wahalhalun da ake fama da su a fadin kasar ba.

Wadannan tsare-tsare guda biyu, kamar yadda suka yi hasashe, ya yi wa tattalin arziki mummunar illar ga talakawa da ma’aikatan Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara