DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ki sanar da mijinki halin da ‘yan Nijeriya ke ciki, sakon Sarkin Kano ga matar Tinubu.

-

 Ki sanar da mijinki halin da ‘yan Nijeriya ke ciki, sakon Sarkin Kano ga matar Tinubu. 

Google search engine

Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero yayi kira ga uwargidan Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ta sanar dashi halin matsi da yan Nijeriya ke ciki. 

Sarkin yayi kiranne yayin wata ziyarar da Remi Tinubu ta kai kano, ya kuma bukaci shugaban kasar da ya gaggauta magance matsalar rashin tsaro a shiyyoyi shida na Nijeriya domin a cewar sa wannan babban kalu balene. 

 

Yace al’ummar kasar nan na cikin mawuyacin hali na matsin rayuwa don haka dole shugabanni su tashi tsaye domin nemowa al’umma mafita. 

Batun rashin tsaro wata babbar matsala ce da gwamnatin Tinubu ta gada amma yakamata gwamnati tayi iyakar kokarinta wajen kwarda matsalar tsaro a fadin kasa. 

Da yake magana kan batun mayar da hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa (FAAN) da wasu ma’aikatun babban bankin Najeriya (CBN) zuwa Legas, Sarkin ya bukaci gwamnatin tarayya da ta fito da tsari na wayar dakan al’umma ta hanyar da zasu gane domin ta hakane za’a samu fahimta tsakanin gwamnati da al’umma. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara