DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bashi ya sa kotu ta kwace kadarar dan takarar gwamna a Kaduna

-

Wata kotun shari’ar Musulunci da ke zamanta a GRA, Zaria jihar Kaduna ta umurci da Hon Sani Sha’aban dan takarar Gwamna a jihar karkashin jam’iyyar ADP a zaben da ya gabata da ya biya bashin Naira milyan 11.2 da wani Alhaji Umar Faruq Abdullahi ke binsa.
Alkalin kotun Alhaji Ishaq Madahu da ya ya ke hukuncin, ya kuma umurci da a kwace kadarar Hon Sani Sha’aban da ya ba da ita a kafin a bashi wancan bashin.
Kazalika, kotun ta umurci da a gaggauta neman wanda zai sayi wannan kadara, domin a biya wannan bashi da ake bin Hon Sani Sha’aban, har kotun ta ce idan kudin wannan kadarar ya zarta kudin bashin da ake binsa, za a maido masa da sauran.
Haka kuma kotun ta umurci Hon Sani da ya yo ciko muddin wannan kadarar ba ta kai yawan kudin da ake binsa ba.
Idan za a tuna dai, an sa hannu kan wata yarjejeniya tsakanin Hon Sani Mahmud Sha’aban (Dan Duran Zazzau) da Alhaji Umar Faruq Abdullahi don fitar da shi (Hon Sha’aban) daga wata matsala a kasar Hadaddiyar Daular Larabawa UAE a shekarar 2018.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara