DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zaman lafiya ya dawo a kananan hukumomi 13 na jihar Katsina – Gwamnati

-

Dikko Umar Raɗɗa 

Mataimakin Gwamnan jihar Katsina Alhaji Faruq Lawan Jobe, ya ce gwamnatin jiha ta yi kokari ta maido da zaman lafiya a kananan hukumomi 13 cikin 22 da ke fama da matsalar tsaro a jihar.

Google search engine

Jaridar This day ta rawaito cewa Faruq Jobe na magana ne a gaban ‘yan jarida, inda ya ce an samu wannan nasarar ne ta dalilin ayyukan jami’an sa kai na ‘Community Watch Corp’ da gwamnatin ta kirkiro, hadin guiwa da sauran jami’an tsaro a jihar.

Daga cikin kananan hukumomin da tsaron ya fara inganta, a ta bakin mataimakin Gwamnan jihar, akwai Batagarawa, Dutsinma, Bindawa, Kusada, Funtua, Danja, Bakori, Malumfashi, Kafur, Musawa, Ingawa, Charanci da Matazu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara