DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu yaki ‘yan bindiga har sai mun ga bayansu – Gwamnatin Katsina

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya ya kai ziyarar jajantawa da ta’aziyya ga al’ummar kauyen Yarnasarawa a cikin karamar hukumar Faskari ta jihar bayan da harin da ‘yan ta’adda suka kai wa kauyen a makon jiya.
Harin ‘yan bindigar dai ya yi sanadiyyar mutuwar mutune 8 kamar yadda sanarwar da daraktan yada labaran ofishin Sakataren Gwamnatin jihar Abdullahi Aliyu Yar’adua ya aike wa DCL Hausa.
Sanarwar ta ce ‘yan bindigar sun farmaki kauyen, inda suka kuma sace mutane 45 da suka hada da mata 37 da maza 8 da mafiyawansu yara ne.
Gwamnan jihar ta Katsina da ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin jihar Abdullahi Garba Faskari, ya nuna jimami, alhini da takaicin abin da ya faru a wannan kauye, inda ya yi ta’aziyya tare da addu’ar Allah Ya gafarta wa wadanda suka rasu.
Gwamnan wanda ya jaddada kudurinsa na ci gaba da yaki da ta’addanci har sai an kawo karshen ayyukan ‘yan ta’adda a jihar, ya kuma bi gida-gida inda ya yi ta’aziyyar wadanda suka rasu.
Sannan Gwamnan ya kuma ziyarci motoci 8 da ‘yan ta’addar suka kona da gidaje 10 da su ma aka kona.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Ficewar Atiku daga PDP ya saba faruwa, muna sa ran zai dawo – Damagum

Shugaban riko na jam’iyyar PDP Ambasada Iliya Damagum, ya bayyana ficewar tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, daga jam’iyyar a matsayin wani lamari da ba...

Mafi Shahara