DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyoyin matasa a a jihar Ogun sun bukaci shugaba Tinubu ya bude boda

-

 Kungiyoyin matasa a a jihar Ogun sun bukaci shugaba Tinubu ya bude boda

Google search engine

Gamayyar kungiyoyin matasan jihar Ogun sun yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya bude dukkanin iyakokin kasa a wani mataki na magance matsalar tsadar abinci da yadda za a kara habaka tattalin arziki da kasar.

Kakakin kungiyar, Fẹmi Owoẹye, wanda ya yi wa manema labarai jawabi a Abeokuta, ya roki Tinubu da ya tashi tsaye wajen shawo kan matsalar ta hanyar bude iyakokin kasa domin bunkasa tattalin arziki da rage tsadar kayan abinci.

Matasan sun kuma nuna damuwarsu kan cewa duk matakan da gwamnati kasar ta bijiro don magance wahalhalun da ake fama da su ba su shafi matasan Nijeriya ba, musamman ma wadanda ba su da aikin yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara