DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai yiyuwar sojojin Nijar su saki Bazoum a Azumin nan

-

 Akwai yiyuwar sojojin Nijar su saki Bazoum a Azumin nan

Google search engine

 Gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar ta ce a shirye take ta amince da sakin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum da matarsa ​​Khadija.

Majiyoyi da dama a Nijeriya da makwabciyarta Nijar, sun tabbatar da shirin gwamnatin mulkin soja na sakin hambararren shugaban kasar a cikin ‘yan kwanaki nan na watan Ramadan.

Sai dai an gano cewa babban abin da ke damun manyan jami’an soji a jamhuriyar Nijar shi ne nacewar Bazoum na cewa zai ci gaba da zama a cikin kasar ta Nijar, bisa dalilin cewa ba ya sha’awar komawa wata kasa daban don ci gaba da rayuwa.

Bazoum na samun goyon bayan shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, sannan kuma shugaban Najeriyar kuma jagoran kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), Bola Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara