DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kaduna ta ce ta ceto daliban Kuriga gaba dayansu

-

A cikin wata sanarwa da Gwamna Uba Sani ya sanya wa hannu, ta yi godiya ga shugaban kasa da jami’an bisa abin da ya ce namijin kokarin da suka yi na ganin an kubutar da daliban ba tare da sun yi ko kwarzane ba.

Duk da dai a sanarwar, Gwamnan bai yi bayanin hanyoyin da aka bi aka ceto daliban ba, amma ya ci gaba da godiya har ga mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da sojoji da daukacin al’ummar Nijeriya da suka yi ta addu’o’in ganin daliban sun kubuta.
A ranar 7 ga wannan wata na Maris ne dai ‘yan bindiga suka shiga makarantar firamaren garin Kuriga na karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna suka yi awon-gaba da dalibai kusan 287.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara