DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta fara gyaran tsohuwar fadar shugaban kasa ta Dodan Barrack da ke Lagos

-

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta sanar da fara gyaran tsohuwar fadar shugaban kasa da ke Dodan Barrack a birnin Lagos.

Gwamnatin ta ce tana da zummar kammala aikin gyaran nan da zuwa 29 ga watan Mayu mai zuwa, 2024 kamar yadda jaridar Punch ta rawaito.
Wani babban jami’in gwamnati da ke da hannu dumu-dumu a cikin aikin gyaran, ya tabbatar da cewa aikin ya zamo wajibi duba yadda ambaliyar ruwa ke barazana ga tsohuwar fadar shugaban kasar, inda har wasu wurare sun fara lalacewa.
Hakan na zuwa ne watanni 4 da shugaban kasa Bola Tinubu ya kasafta kashe Naira bilyan 4 don gyaran gidansa da ke Lagos da kuma gidan mataimakin shugaban kasa shi ma a Naira bilyan 3.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara