DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kisan Sojin Nijar: ECOWAS ta mika wa Janar Tiani goron gayyatar hada gwiwar yaki da ta’addanci

-

 


Google search engine

Daga wakilinmu, Yacouba Maigizawa, Damagaram-Nijar

Kungiyar ECOWAS ta yi Allah wadai da harin da aka kai wa sojojin Nijar da ya sanadiyar rayukan 23 daga cikin su

A cikin wata takarda ce da ta fitar a ranar 23 ga watan nan na Maris, kungiyar ECOWAS ta nuna rashin jin dadin ta da takaici kan harin baya bayan nan a Nijar wanda ya yi awan gaba da rayukan sojojin kasar 23 

Kungiyar ta ce tana isar da sakon ta’aziyar ta ga gwamnati da al’amurar kasar Nijar tare da jaddada goyan bayan ta ga ‘yan uwan mamatan da sojojin kasar

Kazalika sanarwar ta ce kungiyar na fatan kwanciya ta zama hutu ga wadanda suka kwanta damar tare da fatan manzon sauki ga wadanda suka jikkata

A karshe kungiyar cikin kakkausan kalamai ta ce tana tir da Allah wadai da wannan hari na dabbanci ta kuma tabbatar wa hukumomin na Nijar aniyarta ta bada hadin kai wajen yaki da ta’addanci da kuma tsatsaurar ra’ayi a yankin

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara