DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai bukatar Shugaba Tinubu da gwamnoni su kawo daukin gaggawa a karin kudin aikin hajjin 2024 – IHR

-

Kungiyar sa kai da ke kula da ayyukan hajji da Umrah ta Independent Hajj Reporters IHR ta bukaci gwamnatoci a dukkanin matakai da u sa baki don kawo daukin gaggawa don gudun samun karancin mahajjata a aikin hajjin shekarar 2024.
A daren Lahadin nan dai ne hukumar kula da aikin hajjin Nijeriya ta sanar da karin kudin aikin hajjin shekarar 2024.
A cikin wata sanarwa daga shugaban kungiyar ta IHR Alhaji Ibrahim Muhammad da ya aike wa DCL Hausa ta ce kusan kaso 90% na maniyyatan da suka biya kudinsu 4.9m ba su da ikon biyan karin wasu kudi har 1.9m a cikin kwanaki hudu kacal.
A kan haka ne, kungiyar ke kira da babbar murya ga gwamnoni da gwamnatin tarayya da su shiga cikin lamarin don tallafar tsarin don biyan cikon ga maniyyata a matsayin wani tallafi na musamman.
Sanarwar ta buga misali da cewa ko a jihohi za a dauki lokaci mai tsawo kafin ma sakoneya isa ga maniyyatan da suka biya kudinsu ganin cewa Mafi yawansu manoma ne, sannan hakan na iya daukar wani karin lokaci matsakaici kafin maniyyaci ya iya tara kudin da suka kai N1.9m cikin wannan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara