DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Liman ya sauka daga aikin limanci saboda takaddamar kudi N500,000 a Kebbi

-

Babban malamin masallacin juma’a na Wala da ke Birnin Kebbi, Alhaji Rufai Ibrahim ya sauka daga mukaminsa sakamakon takaddamar N500,000 da ta shiga tsakaninsa da na’ibinsa, Malam Mamman Na Ta’ala Yahaya. 
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, Alhaji Ibrahim ya kai karar Malam Yahaya ga hukumar DSS, bayan da ya zarge shi da yin cogen N500,000 daga cikin kudin da ya kamata su raba na kyautar kudin da gwamnan jihar ya ba su, lamarin da ya sanya aka dakatar da shi saboda rashin kai karar ga hukumomin da suka dace. Sai dai daga bisani ya rubuta aje aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara