DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sabon Shugaban kasar Senegal ya nada mai gidansa Fira Ministan kasar.

-

 Sabon shugaban ƙasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, ya naɗa shugaban babbar jam’iyyar adawa, Ousmane Sonko a matsayin firaiministan ƙasar.

Ousmane Sonko dai shi ne ubangidan shugaba Faye a harkokin siyasa kuma an ɗaure su a gidan yari daf da zaɓen na watan Maris.

Google search engine

Amma daga bisani tsohon shugaban ƙasar Macky Sall ya yi masu afuwa, tare da wasu fursunonin siyasa.

Bayan ƴan sa’o’i kaɗan da hawansa mulki a matsayin shugaban ƙasar Senegal ne shugaba Faye ya naɗa Sonko a matsayin firaiminista,” fadar shugaban ƙasar ta wallafa a shafinta na X.

Tun da fari dai an bayyana Sonko a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa amma bayan an kama shi ne sai aka yanke masa hukuncin cewa bai cancanci tsayawa takara ba – matakin da ya haifar da zanga-zanga a faɗin ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara