DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Katsina ya nada sabon shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar

-

Gwamna Radda ya nada Falalu Bawale a matsayin sabon shugaban ma’aikata na Katsina (Head of Civil Service)

Gwamna Dikko Umaru Radda ya amince da nadin Alhaji Falalu Bawale a matsayin shugaban ma’aikata na jihar.
Bawale har zuwa lokacin da aka nada shi a matsayin Shugaban Ma’aikata na Jihar Katsina ya kasance Babban Sakatare a Ofishin Shugaban Ma’aikata na Katsina.
Alhaji Bawale ya karbi mukamin ne daga Alhaji Usman Isyaku wanda ya yi ritaya daga aikin gwamnati bayan ya shafe shekaru 35 yana aiki.
Gwamna Radda ya kuma amince da nadin tsohon shugaban ma’aikata, Alhaji Usman Isyaku a matsayin mai ba da shawara na musamman kan sake fasalin harkokin ma’aikatan gwamnati.
Gwamna Radda ya taya sabon shugaban ma’aikata murnar nadin da aka yi masa, ya kuma bukace shi da ya kawo kwarewa a sabon mukamin da aka nada shi. Ya kuma mika godiyarsa ga shugaban ma’aikata mai barin gado bisa gudunmawar da ya bayar tare da yi masa fatan alheri a kan sabon mukaminsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara