DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsin tattalin arziki ya sa za a rufe kamfanonin sarrafa giya guda biyu a Nijeriya

-

 Matsin tattalin arziki ya sa za a rufe kamfanonin sarrafa giya guda biyu a Nijeriya

Google search engine

Kamfanin samar da giya na Nigerian Breweries na shirin rufe kamfanoni guda biyu,hakan nada nasaba ga ɗimbin matsalolin kuɗi da suke fuskanta, kamfanin ya bayyana hakan a ranar Talata a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Abubuwan da ke damun babban kamfanin sun hada da asarar musayar kudaden waje da aka yi a bara, wanda hakan ya sa ba shi da wani zabi illa rufe biyu daga cikin masana’antun.

Ya bayyana cewa wani babbar asarar da aka yi kan hada-hadar kudaden waje da ya kai Naira biliyan 153.3 ya sanya Kamfanin Breweries na Nijeriya ya yi babbar asara a bara, tun bayan da ya fara aiki shekaru 77 da suka gabata a kasar.

Asarar Naira biliyan 106.3 da aka yi a cikin 2023 ya samo asali ne daga matsalolin tattalin arziki da hauhawar farashin kayayyaki, rashin daidaituwar FX, da sauransu,kamar yadda kamfanin ya bayyana.

An sanar da kungiyoyin kwadagon da suka hada da kungiyar abinci da abin sha da ma’aikatar taba sigari da kuma kungiyar masu shayar da kayan sha da taba sigari kan matakin dakatar da aiki na wani dan lokaci a kamfanonin biyu, a cewar takardar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara