DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku da Wike sun hadu, karon farko tun bayan zaben 2023, sai dai babu tabbacin ko sun gaisa

-

A karon farko tun bayan zaben 2023, Atiku Abubakar da Nyesom Wike sun hadu wajen guda don taron jam’iyyar PDP.

Sai dai Premium Times ta ce babu tabbacin ko sun gaisa a wajen taron.
Atiku Abubakar dai shi ne tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya a zamanin mulkin Olusegun Obasanjo, yayin da Nyesom Wike ya yi Gwamnan jihar Rivers sau biyu, yanzu kuma shi ne ministan Abuja a gwamnatin APC.
Sauran wadanda suka halarci taron akwai tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa Abba Moro da Sanata Aminu Waziri Tambuwal, akwai tsohon Gwamnan jihar Kaduna kuma tsohon shugaban jam’iyyar ta PDP Ahmad Makarfi, da tsohon Gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu, tsohon Gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido da tsohon Gwamnan jihar Plateau Jonah Jang.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara