DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƙirƙirar yan Sandan jihohi zai zama silar ƙãrin sãɓani a tsakanin ƙabilu-Sufeta janar na yan sandan Najeriya

-

Sufeta janar na yan sanda a Najeriya Olukayode Egbetokun ya ce Najeriya bata kai matsayin da zata yi ‘yan sandan jihohi ba saboda za’a riƙa samun umurni daga ɓangarori biyu wato bangaren gwamna da na sufeta janar.

Sufeta janar Olukayode yayi zargin akwai yiyuwar gwamnoni a Najeriya suyi amfani da yan sandan jihohi su wuce gona da iri da kuma take hakkokin yan Adam.

Google search engine

Olukayode Egbetokun ya baiyana cewa jihohi basu da wadãtar da zasu samar da irin ‘yan sandan da ƙasa ke bukata domin a kowace shekara ana buƙatar ɗaukar sãbin yan sanda dubu 30 kamar yadda majalisar ɗinkin Duniya ta bukaci a yi dan samar da ‘yan sanda na zamani.

Ya ce maimakon kirkiro yan sanda na jihohi, ƙãra gwamnati ta haɗe jami’an tsaro na civil defence dana hukumar kare haɗura ta ƙasa road safety wuri guda da yan sanda, ta yadda civil defence ɗin da jami’an roadsafty zasu zamo wasu sassan rundunar yan sanda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara