DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun hallaka shugaban jam’iyyar APC a Katsina

-

Wasu mahara da har lokacin hada wannan labarin ba a tabbatar da adadinsu ba, sun bindige Malam Sai’idu Jikan Basa wanda shi ne shugaban jam’iyyar APC na mazabar Mai Dabino ta karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina.
Majiyar DCL Hausa ta tabbatar mata da cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 3:37 na yammacin Larabar nan a kan hanyarsa daga Danmusa zuwa Mai Dabino.
Bayanai sun ce an kira jiga-jigan jam’iyyar APC na karamar hukumar Danmusa zuwa wani taro a hedikwatar karamar hukumar, inda daga kauyen Mai Dabino ya tafi Danmusa don halartar wannan taro.
Yana kan hanyarsa ta komawa Mai Dabino bayan kammala taron, wannan ibtila’in ya faru da shi, da wani mutumin kauyen Kokarawa da ya rago wa hanya zuwa kasuwar Mai Dabino da ke a ranar Larabar nan.
Majiyar ta ce an yi musu jana’iza bayan sallar la’asar din nan da yammacin Laraba.
Kauyen Mai Dabino na daga cikin yankunan da ke fama da matsalar tsaro da ba su iya shiga hedikwatar karamar hukumar Danmusa sai sun zagaya ta karamar hukumar Kankara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara