DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro a jihar Kebbi sun kama wasu bamabamai da ake ƙoƙarin shigo da su Nijeriya

-

 Jami’an tsaro a jihar Kebbi sun kama wasu bamabamai da ake ƙoƙarin shigo da su Najeriya sakaye a cikin buhuna da kwalaye.

Google search engine

Jami’an tsaron kan iyaka na Hukumar hana fasa kwauri ta Nijeriya Kwastam (NCS) dana hukumar shige da fice ta Nijeriya, Ma’aikatar Harkokin waje da sojojin Nijeriya karkashin jagorancin babban Sufeton Kwastam, A.A. Ibrahim, wanda yanzu mataimakin kwanturola na hukumar Kwastam da ke kan titin Yauri-Jega a jihar Kebbi ya kama kwali 40 da buhuna dauke da ake zargin bama-bamai ne.

Da yake zantawa da manema labarai a jiya a ofishinsa da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi.

Kwanturolan hukumar kwastam na jihar, Iheanacho Ernest Ojike, ya ce bayan gwajin da jami’an hadin gwiwa suka gudanar, an gano kayayyakin da ake zargin dauke da kwalaye 40 da kuma buhuna guda 6,240 na bama-bamai waɗanda akai lodi a kan farar Canter/ babbar mota mai lamba Zur 882ZY tare da lambar babur Haejue JEG-562 UQ.

Kwanturolan ya ce an kama wasu mutane biyu da hukumar kwastam ta tsare su a Birnin Kebbi tare da mika kayayyakin da aka kama ga jami’an tsaro na jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara