DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

-

Cutar kyanda tayi sanadiyyar mutuwar su yara 49 a jihar Adamawa.

Adadin wadanda suka rasa rayukan su sakamakon kamuwa da cutar kyanda a jihar Adamawa ya kai 49.

Google search engine

Hakan ya fito ne a daidai lokacin da jami’an gwamnatin jihar ke bayar da bayanai kan kokarin dakile cutar yayin da hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta yi jawabi ga manema labarai a birnin Yola kan ka’idojin bayar da rahoto na gaskiya kan cutar.

A yayin taron wayar da kai na WHO a ofishin ta na Yola, masanin cutar kanjamau na jihar Adamawa, Kadabiyu Jones, ya ce kawo yanzu an samu rahoton mutuwar mutane 49, yayin da 143 daga cikin 818 da ake zargin sun kamu da cutar kyanda ya tabbatar da sun kamu da cutar.

Ya ce wadanda abin ya shafa yara ne da ke tsakanin shekara 1 zuwa 14, kuma yawancinsu ba a taba yi musu allurar riga-kafi ba.

Ya tabbatar da cewa jihar ta tura jami’an sa ido domin gano bullar cutar kuma tana aiki tukuru don ganin kawo karshen kamuwa da cutar ta hanyar rigakafin da ake yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara