DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ƙwadago ta kudiri aniyar yin zanga-zanga ranar 12 ga watannan na Mayu idan ba’a janye batun karin kuɗin lantarki ba

-

 Kungiyar ƙwadago ta kudiri aniyar yin zanga-zanga ranar 12 ga watannan na Mayu idan ba’a janye batun karin kuɗin lantarki ba

Kungiyoyin kwadago a karkashin inuwar kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC da (TUC) sun rubuta wasikar zanga-zanga zuwa hedikwatar hukumar kula da wutar lantarki ta kasa NERC.

Google search engine

Kungiyar, a cikin wasikar, wacce ke da hadin gwiwar shugaban kungiyar NLC, Comrade Joe Ajaero da shugaban TUC, Comrade Festus Osifo, hadi da sunayen sakataren gwamnatin tarayya (SGF), ministan kwadago da samar da ayyukan yi ta tarayya! Ministan wutar lantarki na tarayya da kamfanonin rarraba wutar lantarki (DISCOs), sun ba da wa’adin ranar 12 ga Mayu, 2024 cewa, NERC ta sauya daga maganar karin kudin wutar lantarki a Nijeriya.

Kungiyoyin biyu sun ba da misali da mawuyacin halin da karin kudin zai tura talakawa a matsayin dalilin kiran a koma baya.

Wasikar ta ce mun yi imanin cewa wannan matakin ba wai kawai abin zargi ba ne idan aka yi la’akari da matsalolin da ‘yan Nijeriya ke fuskanta a halin yanzu,

hakan yasa ba za mu zura ido ba, domin ana cin zarafin talakawa da ma’aikata irin wannan abin da ba za a amince da shi ba.

Wannan dalilin yasa muka rubuta wannan takardar domin ankarar da hukuma cewa muddin ba a janye wannan mataki ba,munshirya tsaf domin gabatar da wannan Zanga-zangar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara