DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin karkatar da kudin ‘yan fansho zuwa wani fanni.

-

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin karkatar da kudin ‘yan fansho zuwa wani fanni.

Gwamnatin tarayya ta musanta zargin da ake cewa tana shirin karbar bashin N20tn na fansho domin bunkasa ababen more rayuwa.

Google search engine

Ministan kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin Nijeriya Wale Edun, ya ce gwamnati za ta bi ka’idojin da aka kafa na asusun fansho domin yin abinda ya dace.

An ruwaito cewa ministan ya shaidawa manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya na kwanaki biyu a fadar shugaban kasa a ranar Talata cewa, gwamnati za ta bayyana shirin yin amfani da kudaden kananan hukumomi da suka hada da asusun don samar da ababen more rayuwa.

Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Alhamis, Edun ya bayyana cewa,harkar fensho, tana da kayyadaddun tsarin doka ta musamman wajen tafiyar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara