DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jirgin farko na alhazan Kano ya tashi zuwa kasa mai tsarki.

-

Jirgin farko na alhazan Kano ya tashi zuwa kasa mai tsarki.

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da jirgin farko na alhazan jihar Kano domin zuwa kasa mai tsarki dan gudanar da aikin hajjin bana.

Google search engine

Solace Base ta rawaito cewa, jirgin ya tashi da misalin karfe 11:41 na safiyar ranar litinin, tare da adadin mahajjata 578 a cikin jirgin Max Air B747 da ma’aikatansa 20, wanda ya nufi filin jirgin sama na Sarki Abdul-Aziz da ke Jeddah.

Gwamna Abba Kabir ya bukaci maniyyatan da su kasance jakadu nagari na jihar da ma Nijeriya a kasa mai tsarki tare da yi wa jihar da kasa baki daya addu’a.

A nasa bangaren, Darakta Janar na Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya ce mahajjatan da ke cikin jirgin sun fito ne daga kananan hukumomi hudu na jihar da suka hada da Gwale,Dala,Fagge da kuma Ungoggo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara