DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mataimakin gwamnan Kano ya janye zargin da ya yiwa Nuhu Ribadu.

-

Mataimakin gwamnan Kano ya janye zargin da ya yiwa Nuhu Ribadu.

Mataimakin gwamnan Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya janye zargin da ya ke yi wa Nuhu Ribadu,mai ba da shawara kan harkokin tsaro kan rikicin masarautar Kano.

Google search engine

Gwarzo ya yi zargin cewa Ribadu ne ya sa aka dawo da Aminu Bayero, wanda aka tube daga sarautar Kano, ta hanyar ba shi jiragen sama guda biyu masu zaman kansu tare da rakiyar jami’an tsaro.

Bayan dawo da Muhammadu Sanusi II,kan karagar mulki,Aminu Ado Bayero ya koma masarautar ranar Asabar,inda ya koma gidan sarki na nassarawa a Jihar.

Gwarzo yace batun cewa an rako tsohon sarki Aminu Ado da jirage biyu tare da rakiyar jami’an tsaro da sukai zargi basu fahimci batun daidai ba.

Sai dai a wata wasika da ya musanta zargin ta hannun lauyoyinsa, Aliyu & Musa Chambers, Ribadu ya bukaci mataimakin gwamnan da ya nemi afuwa.

Wasikar tace wanda suke karewa tare da ofishinsa sun dauki abin da mahimmanci dan haka suna bukatar abasu cikakkiyar hujja akan zargin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara