DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya koka da halin da kananan hukumomi ke ciki a Nijeriya.

-

Tinubu ya koka da halin da kananan hukumomi ke ciki a Nijeriya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nuna damuwarsa kan tabarbarewar harkokin kananan hukumomin kasar nan, yana mai alakanta hakan da koma bayan ci gaba da kuma kasa shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi kasa.

Google search engine

Da yake jawabi a wajen wani taron kasa na kwana guda kan kalubalen tsaro a Nijeriya da kuma shugabanci nagari a matakin kananan hukumomi, shugaban ya jaddada cewa shugabanci nagari a dukkan matakai na da matukar muhimmanci wajen samar da ci gaba da rage rikice-rikice a tsakanin al’umma.

Shugaban wanda ya samu wakilcin Ministan tsaro,Badaru Abubakar, ya ce jihar da ke da kyakkyawan shugabanci ta fi dacewa da magance matsalolin cikin gida kamar yaki da bata gari, tada kayar baya, da rikicin kabilanci da sauransu.

Haka zalika ya ce rashin shugabanci nagari yana haifar da cin hanci da rashawa, rashin zaman lafiya, siyasa, rashin daidaiton tattalin arziki, da kuma tashe-tashen hankula a cikin al’umma wanda ba wai kawai na gurgunta tsaron lafiyar al’umma ta hanyar hana mutane bukatun su na yau da kullun, har ma babbar barazana ce ga tsaron kasa ta hanyar samar da yanayi maikyau ga ‘yan kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara