DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwankwaso ya maka EFCC a kotu

-

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya maka hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC kotu domin hana kama shi.
An gabatar da karar da aka shigar a babbar kotun Kano a gaban mai shari’a Yusuf Ubale.
Wata majiya ta bayyana cewa karar na da nufin hana hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC tsare shi.
Idan dai za a iya tunawa, EFCC na binciken zargin da ake yi wa Kwankwaso kan kudi naira biliyan 2.5 na kudaden yakin neman zabe da ke da alaka da jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a kan Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara