DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

-

Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, 2024 a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokradiyya ta bana.

Google search engine

Ministan harkokin cikin gida, Hon. Dr. Olubunmi Tunji-Ojo shi ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa da babbar sakatariya a ma’aikatar Dr. Aishetu Gogo Ndayako ta fitar.

Ya ce, Yayin da muke bikin ranar dimokuradiyya a cikin tarihin kasarmu mai daraja, bari mu yi tunani a kan kokarin iyayenmu da suka kafa mu kuma tabbatar da cewa Nijeriya ta ci gaba da kasancewa kasa daya, amintacciyar kasa, zaman lafiya da rashin rabuwa.

Yayin da yake taya ‘yan Nijeriya murnar wannan rana, ya bukace su da su dage kan tsarin mulkin dimokradiyya.

Ministan ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kuduri aniyar kawo sauyi mai kyau domin farfado da tattalin arzikin kasa da inganta tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara