DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mahajjaciya daga jihar Borno ta haihu a wani asibiti da ke birnin Makka

-

Mahajjaciya daga jihar Borno ta haihu a wani asibiti da ke birnin Makka

Wata Hajiya ‘yar shekara 30 ta haifi da namiji a wani asibitin kasar Saudiyya dake birnin Makkah.

Google search engine

A cewar kamfanin dillancin labarai na Saudiyya SPA, mahajjaciyar ta isa dakin gaggawa na Asibitin ne bayan ta yi fama da ciwon nakuda.

Nan take jami’an agajin suka duba halin da take ciki sannan suka kaita dakin haihuwa, inda ta haifi yaron nan take.

Yayin da mahaifiyar ke samun sauki, jaririn mai suna Mohammad yana samun kulawa ta musamman, a cikin asibtin.

Kamar yadda jaridar Saudi Gazzet ta ruwaito, wannan shine karo na farko da mahajjaciya ta haihu a lokacin Hajjin shekarar 2024.

A halin da ake ciki, Shugaban Hukumar Kula da Lafiya ta NAHCON na aikin Hajjin 2024 a kasar Saudiyya, Dakta Abubakar Ismail ya tabbatar da cewa Mahajjaciyar mace ‘yar jihar Borno ce.

Ya ce kungiyar likitocin ta kasa ta samu rahoto kan ci gaban da aka samu daga kungiyar likitocin jihar Borno inda ta ce matar ta kaucewa aikin tantance lafiyar da ya wajaba a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara