DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya yi Allah-wadai da harin da ‘yan bindiga suka kai a Katsina

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu da kakkausar murya ya yi Allah-wadai da harin da ‘yan bindiga suka kai a kananan hukumomin Kankara da Dutsinma a jihar Katsina.
Da yake bayyana wannan sabon harin da cewa abin takaici ne, shugaban kasar ya tabbatar da cewa ba zai yi kasa a guiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a da kuma karya lagon masu aikata ta’addanci a sassan kasar.
Shugaban kasar ya umurci jami’an tsaro da su yi dukkanin mai yiwuwa don bi ma wadanda aka halaka hakkinsu ta hanyar yin maganin wadanda suka yi wannan aika-aikar.
Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin jihar Katsina, iyalai da ‘yan’uwan wadanda harin ta’addancin ya rutsa da su, sannan ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa wadanda suka riga mu gidan gaskiya.
Bayanin hakan na kunshe a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Mr Ajuri Ngelale, wanda shi ne Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da DCL Hausa ta samu kwafi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara