DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar kananan hukumomi tace ba za ta iya biyan dubu N62,000 a matsayin mafi karancin albashi ba

-

Kungiyar kananan hukumomi tace ba za ta iya biyan dubu N62,000 a matsayin mafi karancin albashi ba.

Kungiyar Kananan hukumomin Nijeriya (ALGON) ta ce kananan hukumomin kasar ba za su iya biyan mafi karancin albashin da kungiyar kwadagon ke nema ba.

Google search engine

Shugaban kungiyar na kasa, Aminu Muazu-Maifata, ne ya bayyana hakan a wata hira da yayi da gidan talabijin na Channels Television.

Ya ce da kason da ake samu daga asusun gwamnatin tarayya, babu wata karamar hukuma da za ta iya biyan ma’aikata mafi karancin albashi na ₦62,000 da gwamnatin tarayya ke yi balle ma kungiyar kwadagon ta bukaci ₦250,000.

Muazu-Maifata ya ce wasu kananan hukumomin ba su fara biyan ma’aikatan su dubu ₦30,000 da aka amince a matsayin mafi karancin albashi tun a shekarar 2019 ba, kananan hukumomi da dama har yanzu ana biyan ma’aikata ₦18,000 a mafi karancin albashin.

Haka zaka sanya mafi karancin albashi mai yawa haka ba wani abu bane da zai dore domin da dama zai yi musu wahalar biya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara