DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutane uku da ake zarginsu da kai wa yan bindiga makamai da alburusai a jihar Katsina

-

‘Yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutane uku da ake zarginsu da kai wa yan bindiga makamai da alburusai a dazukan jihar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kama wasu mutane uku da ake zargin suna kaiwa ‘yan bindiga makami makamai da alburusai a dajin Katsina.

Google search engine

Wadanda ake zargin su ne sun hada da Haladu Isah na kauyen Tsaskiya, karamar hukumar Safana, Abubakar Ahmed  Sha’iskawa, Barhim, Katsina; da Adamu Musa Ba’ude a Jamhuriyar Nijar.

a cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Katsina, Abubakar Sadiq, kamen ya biyo bayan bayanan da aka samu a ranar 6 ga Afrilu, 2024, a ofishin ‘yan sanda da ke Kaita kan munanan ayyukan mutanen uku.

A wata sanarwa da ya fitar ya ce cikin gaggawar ‘yan sanda sun kai dauki tare da samun nasarar gano wadanda ake zargin tare da cafke su a hanyar Dankama a karamar hukumar Kaita.

an gano wadan da ake zargin a hannunsu da kudi naira miliyan daya da dubu dari biyu da uku (N1,203,000.00k) da ake zargin na alburusai ne

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara