DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Peter Obi yayi kira da al’umma su hada hannu wajen kawo gyara a Nijeriya

-

Peter Obi yayi kira da al’umma su hada hannu wajen kawo gyara a Nijeriya

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi,ya yi kira ga daukacin ‘yan Nijeriya da su hada kai domin kawo sauyi ga al’umma.

Google search engine

Ya kuma yi kira da  shugabanni su dauki mataki domin magance halin da kamfanoni da dama ke ficewa daga Nijeriya, inda ya bayyana cewa hakan yana jawo asarar da aka yi kiyasin Naira tiriliyan 95 cikin shekaru biyar da suka gabata.

Obi, a cikin wata sanarwa daya fitar a shafin sa na X, ya bayyana ficewar manyan kamfanoni goma a cikin shekarar da ta gabata kadai, wadanda suka hada da GlaxoSmithKline, Equinor, Sanofi-Aventis, Bolt Food, Procter & Gamble, Jumia Food, PZ Cussons, Kimberly-Clark, da Diageo.

Yace ya zama dole a magance ficewar da wasu kamfanoni daga Nijeriya ke yi a wannan lokacin domin yana janyo asara ga al’ummar kasar baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara