DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan kano sun tura karin jami’ai zuwa manyan fadojin jihar biyu

-

 Rundunar ‘yan sandan kano sun tura karin jami’ai zuwa manyan fadoji 2 a Kano

Rundunar ‘yan sandan ta tura karin jami’an tsaro zuwa manyan fadadoji guda biyu da ke dauke da sarakunan da ke bangarorin biyu

Google search engine

Tsohon kwamishinan ‘yan sandan Kano, AIG Usaini Gumel ne ya tabbatar da hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ta wayar tarho.

Gumel ya ce, “An tura jami’ai da kayan aiki domin tunkarar duk wani abin da ba a yi tsammani ba a yankunan da aka gano a cikin garin, don haka hukumar .’yan sanda za ta cigaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Ya bayyana cewa tura sojojin na da nufin hana barazanar tsaro da kuma tabbatar da zaman lafiya har sai an samu sakamakon rikicin na masarautar.

AIG Gumel ya ce rundunar ta kara karfafa shirinta na tura jami’anta domin tabbatar da ingantaccen tsaro da zaman lafiya a jihar.

“An baza jami’an tsaro domin tabbatar da tsaro a fadar Kofar Kudu, gidan sarki Malam Mohammadu Sunusi, da kuma fadar Nasarawa Mimi, gidan sarki Aminu Bayero,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara