DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sabuwar kungiyar tawaye a Nijar tace ta ita ce ta yi garkuwa da kantoman Bilma

-

Sabuwar kungiyar tawaye a Nijar ta FPJ ta yi ikirarin cewa ita ce ta yi garkuwa da Kantoman Bilma nan da mukarabbansa

A cikin wani sako ta shafukan sada zumunta, sabuwar kungiyar tawaye ta Front Patriotique pour la Justice ko FPJ a takaice ta ce ita ce ke da alhakin kame shugaban karamar hukumar Bilma da ke cikin jihar Agadez Commandant Amadou TORDA tare da mukarabban sa 4 ciki har da babban jami’in tsaron Gendarmerie na yankin Bilma

Google search engine

Sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Mahamat Tori ta zargi hukumomin mulkin sojan Nijar na CNSP da jefa kasar cikin yanayin kama karya da rashin adalci

A ranar Juma’ar da ta gabata ne 15 ga watan Yunin nan tawagar Kantoman na Bilma a yayin da take kan hanyar ta ta dawowa daga Dirkou bayan halartar wani taron adda’o’in zaman lafiya da kungiyar farar hula ta M62 ta shirya ta fuskanci harin kwantan baunar ‘yan tawayen inda suka budewa tawagar huta nan take lamarin da ya kai ga yin garkuwa da su

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Ficewar Atiku daga PDP ya saba faruwa, muna sa ran zai dawo – Damagum

Shugaban riko na jam’iyyar PDP Ambasada Iliya Damagum, ya bayyana ficewar tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, daga jam’iyyar a matsayin wani lamari da ba...

Mafi Shahara