DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya za ta dakatar da kwangilar aikin hanyar Lokoja da Benin

-

Gwamnatin Nijeriya za ta dakatar da kwangilar aikin hanyar Lokoja da Benin 

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirin dakatar da ayyukan da ‘yan kwangilar ke gudanarwa na gyaran hanyar Lokoja zuwa Benin saboda jinkirin aikin da rashin nuna damuwa da halin da al’ummar yankin ke ciki ga ‘yan kwangilar dake aikin.

Google search engine

Ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki a Uyo,inda ya koka da yadda aikin gyaran hanyar baya sauri.

Ministan kuma ya yi gargadin cewa duk dan kwangilar da ya ci gaba da jan kafa game da aikin da gwamnati ta bashi za’a soke kwangilar sa.

Haka kuma akwai shawarwarin da gwamnatin tarayya ta yi na tallafa wa ‘yan kwangilar dake cikin gida Nijeriya, wanda zai yi  tasiri kai tsaye ga tattalin arzikin masu aikin gaba daya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara