DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sake shiga garin Dutsinma jihar Katsina, sun aike da malamin jami’ar FUDMA lahira

-

Wasu ‘yan bindiga da ba a kai ga tantance adadinsu ba ya zuwa wannan lokaci sun kutsa kai cikin garin Dutsinma na jihar Katsina, inda suka harbe wani malamin jami’ar tarayya ta FUDMA da aka bayyana sunansa da Dr Tiri.
Majiyar DCL Hausa ta kuma ce maharan sun kuma yi awon-gaba da ‘ya’yansa biyu da ba a sanar da jinsinsu ba, wato maza ne ko mata, ko kuma mace da namiji.
Lamarin ya faru a daren Litinin wayewar Talata da misalin karfe 1am.
Majiyar ta ce yanzu haka gawar Dr Tiri da ke koyarwa a sashen tattalin arziki na fannin noma na can a babban asibitin garin Dutsinma jihar Katsina.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ASP Aliyu Abubakar Sadiq bai kai ga amsa kiran wayar da DCL Hausa ta yi masa ba kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara