DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ce ke juya akalar PDP a Nijeriya – Mustapha Inuwa

-

Nyesom Wike da Mustapha Inuwa 

Tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Katsina kuma jigo a jam’iyyar PDP a jihar, Mustapha Muhammad Inuwa, ya zargi jam’iyyar APC da juya akalar jam’iyyar PDP ta hannun ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike.

Inuwa ya bayyana hakan ne a wajen taron masu ruwa da tsaki na ‘ya’yan jam’iyyar PDP a jihar, wanda ya gudana Katsina a karshen mako.

Google search engine

Tsohon sakataren gwamnatin wanda ya yi takarar Gwamna a jam’iyyar APC kafin zaben fitar da gwani, ya kuma zargi wasu ‘ya’yan jam’iyyar ta PDP a jihar da yi mata zagon-kasa.

Yace “Ba su bukatar jam’iyyar ta yi nasara a dukkanin zabuka, su dai burinsu kawai a ce suna takara, idan za a je taron jam’iyya a Abuja su amso kudin ‘daliget’, haka kuma idan za a yi zabe sai su amso kudin zabe, idan za a je kotu, sai su amso kudin su sa aljihu”.

Mustapha Inuwa ya kara da cewa rikicin da jam’iyyar PDP ke ciki a jihar Katsina ƙirƙira shi aka yi, domin wasu dalilai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara