DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku mai dawa ma’aikata kudaden goran sallah da muka basu wanda ku ka karkatar- gwamnan Sokoto

-

 Ku mai dawa ma’aikata kudaden goran sallah da muka basu wanda ku ka karkatar- gwamnan Sokoto

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya umurci jami’an hukumar ilimi na kananan hukumomi da da su mayar wa ma’aikatan jihar da aka karkatar kudin alawus din su na sallah Naira 30,000 ko kuma su fuskanci hukunci.

Google search engine

Gwamnan ya yi wannan gargadin ne a ranar Juma’a a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a da magoya bayansa a gidan gwamnati, da ke sokoto.

Ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda wasu jami’an kudi musamman a matakin kananan hukumomi suka hana ma’aikatan su naira 30,000 da gwamnatin jihar ta amince da aba su a matsayin kyautar Sallah.

Yace wadanda suka karkatar da wadannan kudade dole ne su dawo da su cikin gaggawa idan ba haka ba za mu dauki tsauraran matakan ladabtarwa a kansu.

Za mu tabbatar da cewa masu laifin sun girbi abin da suka shuka domin ya zama izina ga wasu.

Gwamnan ya tuhumi dukkan shugabannin hukumomin da ake tafka ta’asa da cin hanci da rashawa da su gaggauta tattara duk ma’aikatan da abin ya shafa tare da tabbatar da an mayar wa  da mutanen kudadensu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara