DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani Asibiti a jihar Legas ya bayyana cewa suna amsar haihuwar sabbin jarirai 2,500 a kowane wata

-

Wani Asibiti a jihar Legas ya bayyana cewa suna amsar haihuwar sabbin jarirai 2,500 a kowane wata

Google search engine

Babban daraktan asibitin koyarwa na jami’ar jihar Legas (LASUTH), Farfesa Adetokunbo Fabamwo, ya ce sashin kula da masu juna biyu na asibitin suna ansar haihuwar sabbin Jarirai 2,500 a wata.

Fabamwo ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labaran Nijeriya, NAN a Legas.

Yace gidan Ayinke gidane da ake kula da lafiyar mata masu juna biyu da ke cikin harabar asibitin kuma ana yimai lakabi da babban asibitin haihuwa a Nijeriya bayan da aka gyara shi daga maicin gadaje 80 zuwa gadaje 170 da aka samar da na’urorin kiwon lafiya na zamani.

Yace a bangaren ana baiwa mata masu juna biyu ilimin kiwon lafiya a lokacin da ake kula da masu juna biyu sannan kuma ana basu shawarwari kan tsarin iyali da kuma tazarar haihuwa bayan haihuwa a asibitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara