DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Laberiya ya rage albashinsa da kashi 40

-

Shugaban Laberiya ya rage albashinsa da kashi 40%

Shugaban kasar Laberiya Joseph Boakai ya bayyana cewa zai rage albashin da yake karba da kashi 40 cikin dari.

Google search engine

A kwanakin baya ne dai al’ummar kasar Laberiya suka koka bisa tsadar rayuwa da ‘yan kasar ke fama dashi wanda hakan yasa ake bincike kan albashin manyan ma’aikata dake kasar.

Kusan mutane biyar suna iya rayuwa a kasa da $2 (£1.70) a rana a cikin kasar dake yammacin Afirka.

Mista Boakai ya bayyana a watan Fabrairu cewa albashinsa na shekara yakai $13,400 ne,kuma zai rage shi zuwa $ 8,000.

Matakin na Boakai ya yi daidai da na magabacinsa, George Weah, wanda ya rage kashi 25 cikin 100 na albashinsa,wanda

wasu daga cikin al’ummar yammacin Afirka sun yaba da matakin na Mista Boakai, amma wasu na tunanin ko sadaukarwa ce da ganin cewa shi ma yana samun wasu abubuwa kamar alawus-alawus na yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara