DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Filayen jiragen sama uku ne daga cikin 22 ke samun riba a Nijeriya – FAAN

-

Hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta Najeriya FAAN, ta ce filayen tashi uku ne kawai daga cikin filayen jiragen sama 22 da Nijeriya ke samun riba.

Google search engine

Manajan Daraktan FAAN, Olubunmi Kuku ce ta bayyana hakan a ranar Talata yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels.

Ta yi nuni da cewa, ana bayar da tallafin filayen jiragen sama 19 ne saboda ba sa samun zirga-zirgar fasinja daidai da kudin da ake kashewa.

A cewarta, akasarin filayen tashi da saukar jiragen sama 22 da FAAN ke kula da su na bukatar a inganta muhimman ababen more rayuwa a cikin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara