DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu karya farashin kayan abinci a watan Junairu – Gwamnatin Tinubu

-

Ministan harkokin noma na Najeriya Abubakar Kyari yana albashir ga ‘yan Najeriya kan batun karya farashin kayan abinci da gwamnatin shugaba Tinubu ta daura ɗamarar yi a watan Junairu da ke tafe.

Ministan ya ce matakin cire haraji kan wasu kayayyakin abinci ga gwamnatin shugaba Tinubu ta amince wa yan kasuwa shigo da su Najeriya da kuma ƙoƙarin gwamnati na shigo da tan dubu 500 na Alkama da Masara su ne manyan dalilan gwamnati na karya farashin a watan ɗaya na shekara mai zuwa, kuma ya ce gwamnati zata ƙaiyade farashi da za’a riƙa sayar da kayan na abinci.

Google search engine

Kyari ya ce sun samu kwarin gwiwar yin hakanne bayan shawara da ƙungiyar manoman Najeriya ta basu cewa yin hakan ne kadai zai sa a samu saukin rayuwa, saboda a cewar ƙungiyar manoman ta AFAN abinci da ake nomawa ba zai isa ba.

Wannan mataki na gwamnatin tarayya na zuwa shekara guda bayan cire tallafin man fetur, abin da wasu ke ganin kamar ya zo a makare, sannan ina ma ace a wannan lokaci na damuna za’a aiwatar ba wai har nan da kwanaki 180 ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara