DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai shine babbar nasarar da Tinubu ya samu ya zuwa yanzu – Ndume

-

Bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai shine babbar nasarar da Tinubu ya samu ya zuwa yanzu – Ndume

Dan majalisar dattawa mai wakiltar Borno ta Kudu Sanata Ali Ndume, ya ce tabbatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi shi ne babbar nasarar da shugaban kasa Bola Tinubu ya samu tun hawansa mulki a shekarar 2023.

Google search engine

A wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Juma’ar nan, Ndume ya bayyana hukuncin kotun kolin a matsayin babbar nasara da shugaba Tinubu ya samu kawo yanzu tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2023.

Sanatan ya kuma yi kira ga Tinubu da ya gaggauta fara aiwatar da hukuncin kotun ba tare da bata lokaci ba, yana mai cewa dole ne al’ummar kasa su fara jin dadin shugabanci nagari.

Yace tun lokacin da gwamnonin jihohin Nijeriya suka sanya kananan hukumomi a aljihu ake ta samun cece kuce da kuma koma baya ga al’ummar kasa.

Na yi matukar farin ciki da ci gaban da aka samu, kuma ina fatan wannan zai zama farkon samun ‘yancin kananan hukumomi a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara