DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dama sai mun yi wa wasu kananan hukumomi ciko daga aljihunmu – Gwamnonin Nijeriya

-

Dama sai mun yi wa wasu kananan hukumomi ciko daga aljihunmu – Gwamnonin Nijeriya

Kungiyar gwamnonin Nijeriya, sun shirya wani muhimmin taro a mako mai zuwa domin duba hukuncin kotun koli da ta bai wa kananan hukumomin kasar cin gashin kai.

Google search engine

Da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban kasa bayan wata ganawa da kungiyar gwamnonin Nijeriya tayi da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnan jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman, ya ce gwamnonin da ke amfani da dukiyarsu wajen kyautata wa kananan hukumomi sun samu sauki domin an sauke musu wani nauyi.

Shugaban ya kuma tabbatar da cewa gwamnonin jahohin sun ji dadin hukuncin kotun kolin da tayi yace dama can da aljihunan su yawanci suke taimakawa wasu kananan hukumomi.

Yace amma gaba daya, gwamnonin sun ji dadin yadda aka sauke musu nauyin da ke kan su. A cewar sa gaskiya mutane ba su san nawa jihohin ke kashewa wajen ceto kananan hukumomi ba shiyasa ake ta cece kuce kan batun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Nijeriya ta jefa wa hadakar ADC zazzafan martani kan Jana’izar Buhari

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin jam’iyyar ADC cewa Tinubu da jam’iyyar APC na amfani da rasuwar Buhari don samun karbuwar siyasa, tana mai cewa...

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Mafi Shahara