DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fursunoni sun tsere daga gidan yarin Koutoukalé a Jamhuriyar Nijar

-

Rahotanni daga yankin jihar Tillaberi sun tabbatar da tserewar wasu fursunoni da ke tsare a gidan yarin Koutoukalé da ke yankin jihar Tillebari ta Jamhuriyar Nijar.
Bayanan da DCL Hausa ta samu dai na nuni da cewa, gidan yarin na daga cikin gidajen yarin da ke da tsattsauran tsaro kuma mai kunshe da gagga-gaggan ‘yan ta’adda da jagororin su masu hatsarin gaske.
Ma’aikatar cikin gida ta kasar dai tuni ta ce ta ba da umarnin binciko da kuma kamo wadanda suka gudun, don haka ne ma aka ayyana dokar hana zirga-zirga daga bakin karfe 9 na dare a cikin kwaryar birnin Tillaberi.
Gidan yarin Koutoukalé dai da ake kallon sa a mafi tsattsauran tsaro a kasar, dama, an taba dakile wasu hare-hare da ‘yan ta’adda suka kai masa a shekarar 2016 da 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara