DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta bada belin tsohon ministan wutar lantarki kan kudi naira 10bn

-

Kotu ta bada belin tsohon ministan wutar lantarki kan kudi naira 10bn

Mai shari’a James Omotosho na babbar kotun tarayya a Abuja ya bayar da belin tsohon ministan wutar lantarki, Saleh Mamman kan kudi naira biliyan 10 da kuma mutum biyu wadanda za su tsaya masa.

Google search engine

An gurfanar da Mamman ne a kan tuhume-tuhume 12 da ke da alaka da hada baki da badakalar kudade.

A yayin da yake yanke hukunci kan neman belin wanda ake kara, Mai shari’a Omotosho ya ce dole ne wadanda za su tsaya masa su mallaki kadarori a Abuja da mafi karancin kudin da ya kai miliyan N750m.

Kotun ta kuma ce dole ne wadanda za su tsaya masa su mika wa kotun takaddun shaidar biyan haraji na shekaru uku.

Kotun ta yanke hukuncin cewa wadanda zasu tsaya masa sai sun mika bayanan banki da fasfo na kasa da kasa ga kotu.

Daga nan ne kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 25 ga watan Satumba, 2024, domin a fara shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara