DCL Hausa Radio
Kaitsaye

A gidan haya nake zaune a Abuja – Dangote

-

Hamshakin attajirin nan na Nahiyar Afrika Alhaji Aliko Dangote ya ce gidan da yake zaune a duk lokacin da ya ziyarci Abuja, ba nasa bane, haya yake yi.
Aliko Dangote a wata ganawa da manema labarai a Lagos, ya ce irin himmar da yake da ita na ganin masana’antu sun habbaka a Nijeriya ne ya sa baya da burin gina gidaje a wajen kasar.
Dangote ya bayyana cewa ya taba mallaka gida a birnin London amma ya sayar da shi a shekarar 1996.
Ya ce dalilinsa na kin yin gidaje a Amurka ko Ingila shi ne don ya kafa masana’antu kuma ya rage lokacin da zai rika batawa don ziyarar kadarorin da ya adana a kasashen waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Yadda ‘yan cabals ke turawa Buhari takardu a boye don ya sanya musu hannu – Tsohon shugaban ma’aikata, Gambari

Tsohon shugaban ma’aikata na Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana yadda wasu makusantan shugaban suka rika tsallake shi tare da mika takardu...

Mafi Shahara