DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ambaliyar ruwa ta mamaye wasu dakunan karatun dalibai a jami’ar tarayya ta Nassarawa

-

Ambaliyar ruwa ta mamaye wasu dakunan karatun dalibai a jami’ar tarayya ta Nassarawa

Ambaliyar ruwa ta mamaye wasu dakunan karatu a tsangayar koyar da fasaha ta Jami’ar Tarayya ta Lafia a jihar Nasarawa, lamarin da ya kawo cikas ga yin karatu ga daliban a sassan da abin ya shafa.

Google search engine

Wasu dalibai da suka bayyana rashin jin dadinsu kan lamarin,sun bayyana cewa ambaliyar ruwan ta dagula karatunsu sosai, wanda hakan ya sa suke shan wuya wajen gudanar da karatu a zauren da ambaliyar ruwa ta mamaye.

Sun yi kira ga gwamnatocin tarayya da na jihohi da su shawo kan lamarin, musamman ganin yadda jarrabawar su ta gabato. 

Sun yi gargadin cewa ba tare da daukar mataki cikin gaggawa ba, za a iya yin illa ga karatun su tare da ruguza gine-ginen jami’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara