DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai halarci taron hadin kan kasashen Afrika a Ghana

-

Tinubu zai halarci taron hadin kan kasashen Afrika a Ghana

Google search engine

A ranar Asabar din nan ne shugaba Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Accra na kasar Ghana domin halartar taron koli na tsakiyar shekara na kungiyar tarayyar Afirka (AU) karo na shida.

A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan al’umma, Ajuri Ngelele ya fitar ta ce, shugaba Tinubu zai yi jawabi a taron kan matsayin hadin kan yankin a sassa daban-daban na Afirka, inda ya bayyana nasarori da kalubalen da aka fuskanta a yammacin Afirka tun bayan ganawar karshe da aka yi a Nairobi, Kenya, a watan Yuli shekarar 2023.

Shugaba Tinubu wanda shi ne shugaban kungiyar ECOWAS, zai gabatar da ‘Rahoto na 2024 game da halin da al’umma ke ciki, wanda zai mai da hankali kan zaman lafiya, tsaro na yankin Afrika, da gudanar da mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Sokoto za ta bude kofar tuba ga masu tayar da kayar baya dake neman sulhu a jihar

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana aniyar ta na tattaunawa da masu tada kayar baya da ke dauke da makamai wadanda suke shirye domun ajiye makamansu...

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

Mafi Shahara