DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka dena fake wa da Guzuma don ka harbi Karsana – saƙon Ƙungiyar matasa na arewa ga Dele Momodu

-

Ƙungiyar matasa masu ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya ta arewacin Najeriya da ake ƙira Northern Yoths for Peaceful Coexistence ta yi martani mai zafi ga mawallafin jaridar nan ta Ovation Dele Momodu game da buɗaɗɗiyar wasiƙar da ya tura ga shugaban Najeriya Bola Tinubu.

Ƙungiyar ta bakin shugaban ta Haruna Bature, ta ce Mawallafin Dele Momodu yana ƙoƙarin yin amfani da wannan wasika ne kawai don cimma wasu muradun sa, saboda bata ga abin da ya haɗa matsalar tattalin arzikin ƙasa da rikicin jihar Rivers ba da har mawallafin ya hade su wuri guda a wannan wasika yana jana hankalin shugaba Tinubu kan su.

Google search engine

Buɗaɗɗiyar wasiƙar Dele Momodun ga shugaba Tinubu dai an wallafa ta ne a wata Jaridar yanar gizo a makonnan.

Ƙungiyar ta ce Dele Momodu ya fake ne da batun tattalin arzikin ƙasar da biyan buƙatar sa kan batun taƙaddamar siyasar jihar Rivers.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara